Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Ogun ta gurfanar da wasu mutane uku a gaban Kotun Majistare da ke Isabo, Abeokuta, bisa zargin kashe tsohuwar mai gabatar da shirye-shirye a gidan talabijin na Ogun State Television (OGTV), Kitan Oyesiku, da kuma mai tsaronta, Pelumi Adetayo.
Mai magana da yawun rundunar, CSP Babaseyi Oluseyi, ya tabbatar da hakan a ranar Litinin, 6 ga Yuli, 2026.
Ya ce an gurfanar da wadanda ake zargin a Kotun Majistare ta 3 da ke Isabo da misalin karfe 11:30 na safe.
An gurfanar da su ne kasa da makonni biyu bayan da ‘yan sanda suka sanar da cafke su dangane da kisan gillar da aka yi wa Oyesiku da mai tsaronta a gidanta da ke Abeokuta.
Tun da farko, Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Ogun, Bode Ojajuni, ya bayyana cewa bincike ya samu gagarumar nasara ne bayan an gano wata takarda a cikin motar Lexus RX330 da aka sace daga gidan mamaciyar.
Binciken kimiyya da aka gudanar kan takardar ne ya kai jami’an tsaro ga babban wanda ake zargi.
Babban wanda ake zargin, Sodeinde Olajuwon Philip mai shekaru 22, an kama shi ne a ranar 24 ga Yuni a wani wurin aikin gini da ke Ibara a Abeokuta, inda yake aiki a matsayin ma’aikacin gini.
Ci gaba da bincike ya kai ga cafke wasu mutum biyu da ake zargin suna tare da shi, Sakirudeen Abdulraheem Ayoola mai shekaru 27, wanda shi ma mai tsaro ne, da Sobu Obafunsho mai shekaru 36, wanda mason ne.
A cewar ‘yan sanda, Philip ya amsa cewa shi ne ya shirya harin saboda wata tsohuwar gaba da yake yi da Oyesiku tun lokacin da yake aiki a matsayin mai tsaronta. Ya ce manufarsa ita ce ya “koya mata darasi.”
Binciken ya nuna cewa wadanda ake zargin sun fara galaba kan Pelumi Adetayo, mai tsaron da ke bakin aiki a lokacin, kafin su shiga cikin gidan inda suka kashe shi da kuma Oyesiku.
Jami’an bincike sun ce sun tarar da alamun an karya kofar shiga da kuma gwabzawa a wurin da lamarin ya faru. An samu gawar Adetayo a wajen gadin gidan, yayin da aka tarar da gawar Oyesiku a cikin babban gidan.
Daga baya, ‘yan sanda sun gano motar da aka sace ta hanyar amfani da fasahar bibiyar motoci a yankin Onikolobo da ke Jihar Ogun.
Haka kuma, jami’an tsaro sun kwato wasu kayayyakin da ake zargin an yi amfani da su wajen aikata laifin, ciki har da guduma da ta karye, adda, katakon itace da kuma bakin alkalami.
