Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta bayyana cewa shirin Gwamnatin Tarayya na kafa rundunar ‘yan sandan jihohi ba zai zama mafita kai tsaye ga matsalar tsaro da Najeriya ke fuskanta ba.
A cikin wata sanarwa, jam’iyyar ta ce yunƙurin gwamnatin tarayya na yin gyaran kundin tsarin mulki cikin gaggawa domin kafa ‘yan sandan jihohi ya fi kama da martani ga tabarbarewar tsaro fiye da cikakken shiri na gina ingantaccen tsarin aikin ‘yan sanda.
ADC ta jaddada cewa batun kafa ‘yan sandan jihohi ba sabon ra’ayi ba ne, domin an daɗe ana tattauna shi a Najeriya a matsayin wani ɓangare na gyaran kundin tsarin mulki.
Jam’iyyar ta ce abin da ya sauya kawai shi ne yadda gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke ƙoƙarin gabatar da shi a matsayin sabon tsari da kuma mafita ga matsalar tsaron ƙasar.
A cewar ADC, amfanin tsarin ‘yan sandan jihohi zai bayyana ne a nan gaba idan an aiwatar da shi yadda ya kamata, amma ba zai iya warware matsalolin tsaron da ake fama da su yanzu nan take ba.
Jam’iyyar ta kuma soki yadda Majalisar Dokoki ke hanzarta duba kudirin gyaran kundin tsarin mulki, tana mai cewa irin wannan muhimmin sauyi yana buƙatar cikakken tuntuba da tattaunawa da al’umma da masu ruwa da tsaki.
ADC ta tambayi dalilin da ya sa gwamnatin Tinubu ta jira har kusan ƙarshen wa’adinta kafin ta fara hanzarta wannan gyara idan har da gaske ta yi imani da tsarin tun farko.
Jam’iyyar ta ƙara da cewa ko da an amince da dokar, kafa rundunonin ‘yan sandan jihohi zai buƙaci lokaci da kuɗaɗe masu yawa domin ɗaukar ma’aikata, horaswa, samar da kayan aiki, gina cibiyoyi da kuma samar da tsarin sa ido mai zaman kansa.
Haka kuma ta nuna damuwa kan yiwuwar amfani da rundunar ‘yan sandan jihohi wajen murkushe abokan hamayya na siyasa, tana tambayar irin matakan kariyar da za su hana gwamnoni amfani da rundunar ta hanyar da ba ta dace ba.
ADC ta ce dole ne a samar da cikakkun ƙa’idoji kan ɗaukar ma’aikata, gudanarwa, ladabtarwa, kuɗaɗen aiki da kuma sa ido domin kauce wa cin zarafin iko.
Jam’iyyar ta kuma jaddada cewa kafa ‘yan sandan jihohi bai kamata ya maye gurbin gyaran Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ba, domin rundunar ta tarayya za ta ci gaba da taka muhimmiyar rawa wajen yaƙi da ta’addanci, manyan laifukan da suka shafi jihohi da kuma tattara bayanan sirri.
A ƙarshe, ADC ta bayyana cewa za ta goyi bayan duk wani mataki da zai inganta tsaron Najeriya, amma ba za ta amince da matakan da ta kira “wasan siyasa” ba maimakon gina ƙaƙƙarfan cibiyoyin tsaro masu dorewa.
