Wani sabon bincike da Africa Polling Institute (API) tare da tallafin Ford Foundation suka gudanar ya nuna cewa amincewar ‘yan Najeriya ga gwamnati da hukumomin gwamnati na ci gaba da raguwa, duk da cewa haɗin kan al’umma ya samu ɗan ƙaruwa.
Rahoton Nigeria Social Cohesion Survey 2026, wanda aka gabatar a taron National Social Cohesion Dialogue da aka gudanar a Abuja, ya nuna cewa Social Cohesion Index (NSCI) na Najeriya ya kai kashi 48.8%, wanda ya fi na bara da maki biyu, kuma shi ne mafi girma tun lokacin da aka fara gudanar da binciken.
A cewar rahoton da Daraktan API, Farfesa Bell Ihua, ya gabatar, mafi yawan ‘yan Najeriya har yanzu suna da amincewa sosai ga shugabannin addini da na gargajiya, amma ba haka lamarin yake ba ga gwamnati da sauran hukumomin gwamnati.
Binciken ya nuna cewa kashi 51% na ‘yan Najeriya sun bayyana suna amincewa da shugabannin addini, yayin da 45% ke amincewa da shugabannin gargajiya. Sai dai 28% ne kawai suka nuna amincewa da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, yayin da 23% kacal suka ce suna amincewa da Majalisar Dokokin Kasa.
Rahoton ya kuma nuna cewa Majalisar Dokokin Kasa ce ta zama hukuma mafi ƙarancin amincewa a tsakanin jama’a, inda 77% suka bayyana cewa ba su da ko kuma suna da ƙarancin amincewa da ita. Haka kuma 73% sun nuna ƙarancin amincewa da bangaren shari’a.
Duk da haka, binciken ya nuna wasu alamun haɗin kai a tsakanin al’umma. Kashi 71% sun ce a shirye suke su sadaukar da wani abu na kansu domin ci gaban ƙasa, yayin da 77% suka ce za su yi aiki tare da mutane daga sauran ƙabilu domin ƙarfafa haɗin kan Najeriya.
Har ila yau, 89% sun nuna goyon baya ga auratayya tsakanin ƙabilu daban-daban, yayin da 62% suka amince da auratayya tsakanin mabiya addinai daban-daban.
Sai dai rahoton ya nuna cewa 48% na ‘yan Najeriya na ganin ƙasar ta fi rarrabuwa yanzu fiye da shekaru huɗu da suka gabata, yayin da 20% ne kawai ke ganin ƙasar ta fi haɗin kai.
A bangaren daidaito tsakanin maza da mata, 69% sun amince cewa mata ya kamata su samu damar jagoranci a fannoni daban-daban na rayuwa, musamman siyasa da manyan kamfanoni. Haka kuma 62% sun goyi bayan bai wa mata haƙƙin rabon gado daidai da maza.
Binciken ya kuma nuna cewa 45% na ‘yan Najeriya ba su gamsu da rayuwarsu a ƙasar ba, yayin da 55% suka ce idan suka samu dama za su ƙaura zuwa wata ƙasa tare da iyalansu.
API ta shawarci gwamnati da ta ƙara aiwatar da manufofin da za su ƙarfafa haɗin kan ƙasa, da samar da tsarin shugabanci mai haɗa kowa ba tare da nuna bambanci ba.
Har ila yau, cibiyar ta ba da shawarar kafa Hukumar Kula da Haɗin Kan Ƙasa (National Social Cohesion Commission) da kuma kafa sashen kula da haɗin kai a kowace ma’aikata da hukuma ta gwamnati domin inganta zaman lafiya, adalci da haɗin kan al’umma.
