Wata Babbar Kotun Jihar Akwa Ibom ta samu wata mata da laifin yunkurin kashe wata yarinya mai shekaru tara bayan ta yaudare ta daga kasuwa zuwa cikin daji tare da yi mata munanan raunuka.
Yayin shari’ar, yarinyar ta bayyana wa kotu yadda matar ta yaudare ta da cewa wata tsohuwa na son sayen barkononta amma ba za ta iya zuwa kasuwa ba. Ta ce matar ta nemi ta raka ta zuwa wani wuri da ake noman alayyahu domin a biya ta kudin barkonon.
Yarinyar ta ce saboda matar ta kasance cikin kyawawan kaya kuma ta yi mata kama da mutuniyar kirki, sai ta amince ta bi ta.
Ta ce da suka shiga hanyar zuwa cikin daji, sai ta fara jin shakku tare da cewa ba za ta ci gaba da tafiya ba.
A cewarta, matar ta rike ta da karfi, ta daure mata baki da wani yanki na zani domin kada ta yi ihu, sannan ta ciro wuka daga cikin jakarta ta sare mata gefen idon hagu tare da yi mata mummunan rauni a wuya kafin ta tsere.
A nata bangaren, wacce ake tuhuma ta amince cewa ita ce ta fita da yarinyar daga kasuwa zuwa cikin daji, amma ta musanta cewa ita ce ta kai mata harin, tana mai ikirarin cewa ta mika yarinyar ga wata mata da ke aikin noma a wurin.
Sai dai alkalin kotun ya bayyana cewa wacce ake tuhuma ta kasa bayyana sunan, adireshi ko wata shaida da za ta tabbatar da wanzuwar matar da take ikirarin ta mika wa yarinyar.
Kotun ta ce hujjojin da masu gabatar da kara suka gabatar sun tabbatar ba tare da shakka ba cewa ita ce ta yaudari yarinyar zuwa cikin daji tare da kai mata harin.
Alkalin ya kara da cewa irin raunukan da aka yi wa yarinyar, musamman sara a wuya da kuma kokarin lalata mata ido, sun nuna cewa an yi harin ne da niyyar kashe ta.
Kotun ta jaddada cewa tsira da yarinyar ta yi ba ya canja gaskiyar cewa wanda ya kai mata harin yana da niyyar kashe ta.
Bayan nazarin shaidu da hujjoji, kotun ta yanke hukuncin cewa wacce ake tuhuma tana da laifin yunkurin kisan kai.
