Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Ekiti ta kama wani mutum mai suna Sunday Olawale bisa zarginsa da yaɗa labarin ƙarya a kafafen sada zumunta cewa ‘yan bindiga sun kai hari garin Are Ekiti da ke ƙaramar hukumar Irepodun Ifelodun.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Sunday Abutu, ya bayyana cewa bincike ya tabbatar da cewa labarin ba gaskiya ba ne, inda wanda ake zargin ya amsa laifin yada bayanan da suka jefa jama’a cikin fargaba.
A cewarsa, an kama Olawale ne bayan jami’an rundunar sun gano shi a yankin Ekute da ke Ado Ekiti, inda ake zarginsa da aikata laifin yaɗa bayanan ƙarya da ka iya haddasa rikici da karya doka da oda.
Rundunar ta sake jaddada cewa babu wani hari da ‘yan bindiga suka kai a Are Ekiti ko wani bangare na jihar, tare da kira ga jama’a da su rika tantance sahihancin bayanai kafin yada su.
Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar, Michael Falade, ya gargadi masu yada labaran ƙarya cewa rundunar ba za ta lamunci duk wani yunkuri na tayar da hankalin jama’a ta hanyar yada bayanan karya ba.
Ya kuma bukaci al’umma su rika amfani da kafafen sada zumunta cikin hankali tare da tabbatar da gaskiyar duk wani bayani kafin su yada shi ga wasu.
