Dan takarar gwamnan jihar Sokoto na jam’iyyar ADC, Dan’iya, ya bayyana cewa idan aka zabe shi, gwamnatinsa za ta mayar da hankali wajen gyara harkokin aikin gwamnati, yaki da talauci da kuma inganta rayuwar al’ummar jihar.
Dan’iya ya nuna damuwa kan rahotannin da ke cewa wasu ma’aikatan gwamnati da na kananan hukumomi sun fuskanci matsaloli a aikinsu saboda alakarsu da gwamnatocin baya.
Ya ce aikin gwamnati ya kamata ya kasance bisa kwarewa, cancanta da bin doka, ba wai la’akari da siyasa ba.
“Aiki na gwamnati abu ne mai dorewa. Ma’aikatan gwamnati bayi ne na jiha, ba na wata jam’iyyar siyasa ba. Duk wata gwamnati da ke son ci gaba mai dorewa dole ta mutunta kwarewa, gogewa da cancanta,” in ji shi.
Dan takarar ya ce gwamnatinsa za ta mayar da hankali wajen magance matsalolin talauci, rashin aikin yi, ilimi, kiwon lafiya da ci gaban karkara.
Ya yi nuni da rahotannin Hukumar Kididdiga ta Kasa (NBS) da kuma National Multidimensional Poverty Index, wadanda suka nuna cewa jihar Sokoto na cikin jihohin da ke fama da matsanancin talauci a Najeriya.
A cewarsa, talauci ba wai rashin kuɗi kaɗai ba ne, har da rashin ingantaccen ilimi, lafiya, abinci mai gina jiki, matsuguni, wutar lantarki, tsafta da tsaftataccen ruwan sha.
“Dole ne gwamnati ta mayar da hankali wajen fitar da jama’a daga talauci, samar da damammaki da kuma inganta rayuwar al’umma. Burinmu shi ne dawo da fata da samar da mafita ga matsalolin jama’a,” ya bayyana.
Dan’iya ya kuma tabbatar wa ma’aikatan gwamnati cewa zai ba da fifiko ga gyaran tsarin aiki, horar da ma’aikata, bunkasa ƙwarewarsu da kuma biyan hakkokinsu a kan lokaci.
Haka kuma ya yi alkawarin gina tsarin aikin gwamnati na zamani wanda zai kasance bisa cancanta da amfani da fasaha domin ya yi gogayya da mafi kyawun cibiyoyin gwamnati a ƙasar nan.
Tun da farko, Malam Muhammad Gumbi, wanda ya jagoranci tawagar da ta kai masa ziyara, ya taya Dan’iya murnar Sallah tare da bayyana goyon bayansu ga jam’iyyar ADC da manufofinta na samar da gwamnati mai adalci, gaskiya da ci gaba a jihar Sokoto.
Ya ce suna da yakinin cewa Dan’iya zai aiwatar da sauye-sauyen da za su karfafa aikin gwamnati da inganta shugabanci idan aka zabe shi a shekarar 2027.
