Wani bangare na jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ya yi watsi da ikirarin cewa akwai gibi a shugabancin jam’iyyar bayan hukuncin da Kotun Koli ta yanke kwanan nan, yana mai cewa har yanzu Abdulrahman Mohammed ne ke ci gaba da zama Shugaban jam’iyyar na kasa, tare da Samuel Anyanwu a matsayin Sakatare na kasa.
Mai magana da yawun bangaren, Jungudo Mohammed, ya bayyana hakan ne yayin taron manema labarai da aka gudanar a Wadata Plaza da ke Abuja ranar Juma’a.
Ya ce wa’adin Adolphus Wabara a matsayin shugaban kwamitin amintattu (BoT) ya riga ya kare tun kafin rikicin da ake ciki yanzu, yana mai gargadin cewa ba za su lamunci duk wata magana da ta saba da haka ba.
Mohammed ya zargi Tanimu Turaki (SAN), Wabara, Ini Ememobong da wasu da karkatar da gaskiya tare da yaɗa bayanan karya game da hukuncin Kotun Koli da aka yanke ranar 30 ga Afrilu, 2026.
A cewarsa, hukuncin Kotun Kolin ya soke babban taron jam’iyyar na Ibadan ne kawai, tare da yin watsi da ƙarar da kwamitin Turaki ya shigar saboda rashin cancanta.
“Wannan shi ne ainihin hukuncin kotun, sabanin yadda wasu ke ƙoƙarin yaɗa ƙarya. Kotun ba ta tabbatar da dakatarwa ko korar wani jami’in jam’iyya ba,” in ji shi.
Ya kara da cewa babu wani gibi ko cikas a shugabancin PDP da zai sa wani bangare ya karɓi ragamar mulki.
“Tsarin shugabancin PDP yana nan daram, bisa doka kuma yana aiki ƙarƙashin Abdulrahman Mohammed da Samuel Anyanwu,” ya jaddada.
Mohammed ya kuma bayyana ikirarin cewa kwamitin amintattu ya karɓi jagorancin jam’iyyar a matsayin abin da babu tanadi a kundin tsarin mulkin jam’iyyar da ya amince da shi.
Ya ce:
“Abin mamaki shi ne yadda Sanata Adolphus Wabara, wanda wa’adinsa ya kare, ke ikirarin jagoranci. Shugabancin BoT na halal shi ne wanda Sanata Mao Ohuabunwa ke jagoranta.”
A gefe guda, Kotun Koli ta Najeriya ta soke babban taron PDP na kasa da aka gudanar a Ibadan a watan Nuwamba 2025, wanda ya samar da shugabancin Tanimu Turaki mai goyon bayan Gwamnan Oyo, Seyi Makinde.
Kotun ta bayyana cewa taron ya saba da umarnin kotu da aka bayar tun farko.
Tun da farko, Wabara ya bayyana cewa babu sahihin shugabanci a jam’iyyar, yana mai cewa BoT ne zai karɓi jagoranci domin dawo da zaman lafiya a PDP.
