Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta sanar da fara nuna kundin rajistar masu kada kuri’a na farko (Preliminary Register of Voters) a dukkanin kananan hukumomi 20 na Jihar Bauchi.
Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban bangaren wayar da kan masu zabe da hulda da jama’a na hukumar a jihar, Aliyu Hassan-Shaba, ya fitar a Bauchi ranar Alhamis.
A cewarsa, za a gudanar da wannan muhimmin aiki daga ranar 29 ga Afrilu zuwa 5 ga Mayu, 2026, domin bai wa al’umma damar tantance bayanansu.
Hassan-Shaba ya bayyana cewa wannan shiri zai ba wa ‘yan kasa damar duba cikakkun bayanansu domin gyara duk wata kuskure da aka samu yayin rajista.
Ya kara da cewa wannan dama za ta kuma bai wa jama’a ikon kai korafi kan sunayen:
Wadanda suka mutu
Baki ko ‘yan kasashen waje
Kananan yara da ba su kai shekarun kada kuri’a ba
domin cire su daga kundin rajistar masu zabe.
Hukumar ta bukaci wadanda suka yi rajista a zangon biyu na aikin su tabbatar da duba bayanansu sosai tare da sanar da INEC duk wata matsala ko kuskure domin tabbatar da sahihancin kundin rajistar kasa baki daya.
INEC ta jaddada cewa wannan mataki yana da matukar muhimmanci wajen tabbatar da ingancin tsarin zabe, gaskiya, da kuma tabbatar da cewa sahihan masu kada kuri’a ne kadai ke cikin rajista.
Masu ruwa da tsaki sun bayyana wannan shiri a matsayin wani muhimmin bangare na karfafa dimokuradiyya da tabbatar da sahihin zabe a jihar Bauchi da kasa baki daya.
Hukumar ta kuma shawarci al’umma da su yi anfani da wannan dama kafin wa’adin da aka kayyade ya kare.
