Ministar Harkokin Mata, Hajiya Imaan Suleiman-Ibrahim, ta bayyana cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bai wa Ma’aikatarta gagarumin goyon baya domin ƙarfafawa mata a Arewacin Najeriya da sauran sassan ƙasar.
Ta bayyana hakan ne a lokacin gabatar da jawabi a taron kwanaki biyu da Gidauniyar Tunawa da Sir Ahmadu Bello ta shirya a Kaduna, domin tattaunawa tsakanin gwamnati da ’yan ƙasa.
Ministar ta ce goyon bayan da Shugaba Tinubu ya bai wa ma’aikatar ya ba su damar farfaɗo da aikace-aikacen da suka shafi mata da iyalai.
Ta jaddada cewa da yawa daga cikin dokokin da ke kare haƙƙin yara da mata sun tsufa, kamar dokar haƙƙin yara da ta kai shekaru 30, da kuma VAAP Act da ke da shekaru 10.
Ta ce ana sake duba waɗannan dokoki da manufofi domin daidaita su da zamani da kuma yawaitar matsaloli kamar cin zarafin mata da kuma mummunar dabi’ar lalata da yara.
Hajiya Imaan ta ƙara da cewa Ma’aikatarta za ta haɗa hannu da Ma’aikatar Kasuwanci da Zuba Jari da kuma Ƙungiyar Masana’antu domin fayyace kasuwancin da mata ke jagoranta.
Wannan haɗin gwiwar, a cewarta, zai taimaka wajen ƙirƙirar manufofi masu amfani da za su inganta rayuwar mata a fadin Najeriya.