Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta bai wa tsohon Manajan Daraktan Warri Refining and Petrochemical Company Limited, Jimoh Yisawu, belin naira miliyan 500 yayin da yake fuskantar shari’a kan tuhume-tuhume takwas da suka shafi zargin wankin kuɗi.
Yisawu ya musanta dukkan tuhume-tuhumen bayan an karanta masa su a gaban Mai Shari’a Inyang Ekwo.
Gwamnatin Tarayya ce ta shigar da ƙarar, tana zarginsa da karya dokokin Money Laundering (Prevention and Prohibition) Act, 2022.
A cewar masu gabatar da ƙara, ana zargin Yisawu da karkatar da sama da dalar Amurka $789,950 da ake zargin kuɗaɗen da aka samu ta haramtacciyar hanya ne. Haka kuma ana zarginsa da biyan kuɗaɗe masu yawa ta hannu ba tare da amfani da banki ba, lamarin da ya saɓa wa dokar hana wankin kuɗi.
Lauyan gwamnati, Ekele Iheanacho (SAN), ya buƙaci kotu ta ƙi bayar da beli, yayin da lauyan wanda ake ƙara, Wale Balogun (SAN), ya roƙi kotu ta ci gaba da sharudan belin da hukumomin bincike suka ba shi tun farko.
A hukuncinsa, Mai Shari’a Inyang Ekwo ya ce wanda ake tuhuma yana da damar samun beli, inda ya sanya sharadin biyan naira miliyan 500 tare da mutum guda da zai tsaya masa mai irin wannan ƙima.
Kotun ta kuma umarci wanda zai tsaya masa ya kasance ɗan Najeriya mai kadarar ƙasa a Abuja, tare da gabatar da takardun mallakar kadarar ga magatakardar kotu.
Haka kuma, kotun ta umurci Yisawu da ya miƙa fasfo ɗinsa na ƙasa da ƙasa ga kotu, tare da hana shi fita daga Najeriya ba tare da izinin kotu ba.
Sai dai kotun ta ce zai ci gaba da kasancewa a hannun masu gabatar da ƙara har sai ya cika dukkan sharudan belin.
An ɗage ci gaba da sauraron shari’ar zuwa ranakun 25, 26 da 27 ga Oktoba, 2026.
