Gwamnatin Tarayya ta sanar da cewa za ta fara girke kusan hasumiyoyin sadarwa 3,700 a faɗin Najeriya daga watan Oktoban 2026, domin faɗaɗa hanyoyin sadarwa da haɗa fiye da mutane miliyan 20 da ke zaune a yankunan da ba su da ingantacciyar hanyar sadarwa.
Ministan Sadarwa, Ƙirƙire-Ƙirƙire da Tattalin Arzikin Zamani, Dr. Bosun Tijani, ne ya bayyana hakan yayin gabatar da shirye-shiryen gwamnati na bunƙasa ababen more rayuwa na fasahar sadarwa.
A cewarsa, wannan shiri na daga cikin manyan ayyukan da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke aiwatarwa domin rage gibin fasahar sadarwa tsakanin birane da karkara.
Tijani ya ce bayan watanni ana tsara aikin da kuma neman kuɗaɗen aiwatar da shi, yanzu an kai matakin fara aiwatarwa bayan samun amincewar shugaban ƙasa.
Ya bayyana cewa hasumiyoyin za su samar da damar amfani da wayar hannu da intanet ga miliyoyin ‘yan Najeriya da ke zaune a ƙauyuka da yankunan da ke da wahalar samun sadarwa.
Ministan ya ƙara da cewa aikin zai taimaka wajen cika burin gwamnati na shimfiɗa kilomita 90,000 na igiyoyin fibre optic a faɗin ƙasar domin ƙara saurin intanet da inganta hanyoyin sadarwa.
Ya ce wannan aikin zai shafi dukkan yankunan siyasa shida, jihohi 36, ƙananan hukumomi da ma gundumomi a Najeriya.
A cewarsa, sauye-sauyen manufofi da gwamnatin Tinubu ta aiwatar, ciki har da ayyana kayayyakin sadarwa a matsayin muhimman ababen more rayuwa na ƙasa, gyaran harajin kamfanonin sadarwa da daidaita wasu kuɗaɗen haraji, sun taimaka wajen bunƙasa fannin.
Tijani ya ce fannin tattalin arzikin zamani yanzu yana bayar da gudunmawar kusan kashi 21 cikin 100 ga tattalin arzikin Najeriya.
Haka kuma, ya sanar da cewa gwamnatin tarayya na shirin ƙaddamar da sabon tsarin adireshin gidan waya na zamani (alphanumeric postcode system) daga ranar 1 ga Oktoba, 2026, wanda zai bai wa kowane gida da kadara a Najeriya adireshin dijital na musamman domin sauƙaƙa harkokin kasuwanci, jigilar kaya, ayyukan gaggawa da sauran hidimomin gwamnati.
Aikin girke hasumiyoyin sadarwar na daga cikin shirin Nigeria Universal Communication Access Project (NUCAP), wanda ke da nufin samar da hanyoyin sadarwa masu amfani da makamashi mai tsafta ga al’ummomin karkara da yankunan da ke da wahalar isa.
