Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya bayyana cewa sauye-sauyen da gwamnatinsa ta aiwatar sun kara karfafa tattalin arzikin jihar tare da inganta ayyukan yi wa jama’a hidima.
Gwamnan ya bayyana hakan ne lokacin da ya karbi bakuncin tawagar Hukumar Rarraba Kudin Shiga da Tsare-tsaren Kudi ta Kasa (RMAFC), karkashin jagorancin shugabanta, Dakta Mohammed Bello Shehu, a gidan gwamnatin jihar.
Uba Sani ya ce gwamnatin sa ta samu nasarori wajen kara kudaden shiga na cikin gida (IGR) ta hanyar amfani da fasaha, inganta tsarin karbar haraji da kuma tabbatar da gaskiya wajen tafiyar da kudaden gwamnati.
Ya bayyana cewa shirin Project C.R.A.F.T. da dandalin PAYKADUNA sun taimaka wajen saukaka biyan kudaden gwamnati tare da rage asarar kudaden shiga.
A bangaren lafiya, gwamnan ya ce an inganta cibiyar lafiya guda daya a kowace karamar hukuma zuwa cibiyar nagarta, an samar da sabbin kayan aikin likitanci, motocin daukar marasa lafiya da kuma inganta walwalar ma’aikatan lafiya.
Game da ilimi kuwa, ya ce gwamnatin jihar ta ware kashi 26.5 cikin 100 na kasafin kudi ga bangaren ilimi, tare da fadada shirye-shiryen ciyar da dalibai da ilimin kyauta.
Uba Sani ya kuma bayyana cewa yawan yaran da ba sa zuwa makaranta ya ragu daga kimanin 535,000 a shekarar 2023 zuwa 187,720 bayan sabon binciken da gwamnati ta gudanar.
Ya ce wadannan nasarori sun samu ne sakamakon kyakkyawan tsarin tafiyar da kudi, jajircewar gwamnati da kuma saka hannun jari wajen bunkasa rayuwar al’umma.
