Close Menu
  • Home
  • News
    • National
    • International
  • Asrah 24 TV
  • Education
  • Health
  • Podcast
  • Politics
  • Sports
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
Facebook X (Twitter) YouTube WhatsApp Telegram
Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
ASRAH 24 MEDIA
Subscribe
  • Home
  • News
    1. National
    2. International
    3. View All

    Najeriya Ta Kai Dala $18.4 Biliyan a Cinikayyar Cikin Afirka a 2024

    June 28, 2025

    Afreximbank Ta Ba Najeriya Tallafin $50 Biliyan Don Manyan Ayyuka

    June 28, 2025

    Mutane 28 sun mutu sakamakon gudun wuce sa’a a jihar Ondo- FRSC

    February 2, 2025

    Najeriya Ta Fuskanci Limit na Visa zuwa Amurka – 3 Mako Kaɗai!

    July 9, 2025

    Gwamnatin Tarayya Tare da Faransa Za Su Inganta ICT a Jami’o’in Najeriya da Tallafin Naira Biliyan 38

    July 4, 2025

    Zafin Rana Mai Tsanani Ya Ɓarke a Turai: Matsalar Heat Dome

    June 30, 2025

    Najeriya Ta Samu Jarin Waje Har Dala Biliyan 2.5 Daga Masarautar Saudiyya

    June 29, 2025

    Jihohi sun raba Naira biliyan 22.9 a matsayin kudin gyaran muhalli

    September 1, 2025

    Gwamna Bago Ya Rusa Majalisar Ministocinsa a Neja

    September 1, 2025

    Atiku Ya Bukaci Jam’iyyun Adawa Su Ƙi Karɓar Sakamakon Zaɓen Rivers

    September 1, 2025

    Tinubu ya na adalci ga kowanne yanki na ƙasar nan – Ministan Yaɗa Labarai

    September 1, 2025
  • Asrah 24 TV
  • Education

    Ƴar Najeriya ta lashe gasar iya Turanci ta duniya a London

    August 5, 2025

    Yan Kano 3 Sun Yi Nasarar Lashe Gasar Nazarin Tarihin Shehu Usman Dan Fodio A Najeriya Wani gagarumin farin ciki ya bayyana a jihar Kano bayan dalibai uku daga makarantar Rumfa College suka lashe gasar kasa ta nazarin tarihin Shehu Usman Dan Fodio da aka gudanar a Abuja. Gasar wadda ta haɗa jihohi 17 na Arewa, ta nuna hazakar matasan Kano inda suka samu kashi 96% na maki gabaɗaya. > “Mun yi nasara ne saboda muna jin dadin tarihinmu. Shehu Dan Fodio ya ba mu abin alfahari,” in ji ɗaya daga cikin daliban da suka yi nasara. Gwamnatin Kano ta sha alwashin ba su kyautar karatu da tallafi na musam

    August 1, 2025

    NSUBEB ta Bukaci ‘Yan NYSC su Auri Mutane a Jihar Nasarawa

    July 10, 2025

    Ɗalibar Najeriya Ta Lashe Gwarzon Daliba A Oxford

    June 29, 2025

    Gwamnatin Kano ta baiwa dalibai hutun bikin Sallah Babba

    June 1, 2025
  • Health

    WHO Ta Tabbatar Da Sabon Magani Mai Karfi Akan Ciwon Sikila da Sankarau

    June 29, 2025

    Gwamnatin Najeriya za ta fara bada agajin gaggawa kyauta ga marasa Lafiya a Kano

    May 17, 2025

    Cutar Zazzabin Lassa Ta Hallaka Mutane 80 a Najeriya Cikin Mako Daya

    February 25, 2025

    Mutane 28 sun mutu sakamakon gudun wuce sa’a a jihar Ondo- FRSC

    February 2, 2025
  • Podcast
  • Politics

    Gwamnatin Kano Ta Kaddamar da Yakin Kakkabe Malaria

    July 30, 2025

    Keyamo ya Caccaki Atiku kan Sauya Sheka a Lokacin Makokin Rasuwar Buhari

    July 17, 2025

    Gwamna Abba Yusuf Ya Nada Sabon Chief of Staff da DG Special Services

    July 13, 2025

    Gwamnatin Kano Na Neman Ƙara Jiha Guda da Kananan Hukumomi 26

    July 13, 2025

    Yabo Gagarumi Ga Gwamna Abba Yusuf Kan Tsare-Tsaren Hajjin Bana

    July 13, 2025
  • Sports

    Ahmed Musa Ya Yi Alkawarin Dawo da Kano Pillars Zuwa Matsayinta na Gaba da Gaba a Afrika

    July 10, 2025

    Tsohon Goalkeeper Peter Rufai Ya Rasu

    July 4, 2025

    Najeriya ta doke kasar Egyp da ci 4-1: U-20 AFCON

    May 19, 2025

    FIFA ta amince da kasashe 48 su halarci gasar cin kofin Duniya ta Mata a shekarar 2031

    May 10, 2025

    Flying Eagles ta doke kasar Egyp a shirye-shiryen fara tun karar gasar AFCON

    April 23, 2025
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
ASRAH 24 MEDIA
Home » Dalilin da ya sa gwamnan Abba na Kano ya kori wasu hadimansa 2
News

Dalilin da ya sa gwamnan Abba na Kano ya kori wasu hadimansa 2

Asrah24 MediaBy Asrah24 MediaAugust 10, 20253 Mins Read
Facebook Twitter WhatsApp

IMG 2537Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya kori wasu hadimansa biyi masu taimaka masa na musamman biyo bayan sakamakon kwamitin bincike da aka kafa domin bincikar kowannensu.

Wanann na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar Kano, Umar Farouk Ibrahim, ya fitar a ranar Asabar.

Sakamakon wancan bincike, gwamnan ya amince da sallamar Abubakar Umar Sharada, babban mai taimaka masa kan harkokin siyasa bayan kwamitin bincike ya same shi da hannu wajen belin babban dilan ƙwaya Sulaiman Aminu Danwawu.

Kwamitin ya bankaɗo yadda Sharada ya bayar da shaida ta ƙashin kansa kan wannan gagarun dilan kwayan.

A cewar wasiƙar da sakataren gwamnatin Kano (SSG), ya fitar a ranar Juma’a, 8 ga Agustan 2025, an buƙaci Sharada ya miƙa dukkan kayan gwamnati da ke hannunsa ga sakataren dindin na ofishin mai bincike da tantancewa da harkokin siyasa (REPA) da ke ƙarƙashin ofishin sakataren gwamnatin, a ranar ko kafin Litinin, 11 ga watan Agustan 2025.

Sannan ana gargaɗinsa da kiran kansa da jami’an wannan gwamnati a ko’inna.

Haka kuma, gwamnan Kano ya sauke Tasiu Adamu Al’amin Roba, babban mai taimaka masa kan tafiyar da al’amuran gwamnat (Cabinet Office) bayan samunsa da laifin sauya buhunhunan hatsi na tallafi da ke ajiye a ɗakin ajiya a Sharaɗa tun a shekarar 2024.

Tun wannan lokaci ne Roba ke fuskantar shari’a a kotu bisa zargin laifin sata da haɗa kai wajen aikata babban laifi na karkatar da kayan gwamnati.

Shi ma Roba, an buƙaci ya miƙa duk wani abin amfani na gwamnati da ke hannunsa haɗi da shaidar fayyace kai (ID card) , a ranar ko kafin Litinin 11 ga watan Agustan 2025. Sannan ana gargaɗinsa da kauce wa kiran kansa da jami’in gwamnatin jihar Kano.

A wani makamancin al’amari, gwamnatin Kano ta wanke Hon. Musa Ado Tsamiya, babban mai taimaka wa gwamna kan magudanan ruwa daga zargin da ake yi masa wanda kwamitin binciken ya tabbatar cewa bai aikata kowanne irin laifi.

Gwamna Abba ya jaddada aniyar gwamnatinsa ta tabbatar da ɗa’a da gaskiya da cewa ba za ta lamunci kowanne irin nau’i na cin hanci da rashawa ba.

Ya kuma gargaɗi dukkan masu riƙe da muƙamai da yi riƙo da gaskiya a dukkan ayyukansu da suka shafi gwamnati da kuma na ƙashin kansu.

“Da wannan sanarwa, ana shawartar al’umma da su guje wa yin kowacce iriyar mu’amala da tsofaffin masu taimaka wa gwamnan da aka kora, musamman abin da ya shafi gwamnati. Kuma duk wanda ya yi hakan, to kar ya zargi kowa, sai kansa.

Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp
Previous ArticleMatatar man Ɗangote ta tarwatsa harkar shigo da tataccen mai Najeriya daga Belgium -Jakadan Belgium
Next Article wuce’Har yanzu Peter Obi ɗan Jam’iyyar Labour ne’

Related Posts

Jihohi sun raba Naira biliyan 22.9 a matsayin kudin gyaran muhalli

September 1, 2025

Gwamna Bago Ya Rusa Majalisar Ministocinsa a Neja

September 1, 2025

Atiku Ya Bukaci Jam’iyyun Adawa Su Ƙi Karɓar Sakamakon Zaɓen Rivers

September 1, 2025

Tinubu ya na adalci ga kowanne yanki na ƙasar nan – Ministan Yaɗa Labarai

September 1, 2025
Add A Comment
Leave A Reply Cancel Reply

Latest Posts

Jihohi sun raba Naira biliyan 22.9 a matsayin kudin gyaran muhalli

September 1, 2025

Gwamna Bago Ya Rusa Majalisar Ministocinsa a Neja

September 1, 2025

Atiku Ya Bukaci Jam’iyyun Adawa Su Ƙi Karɓar Sakamakon Zaɓen Rivers

September 1, 2025

Tinubu ya na adalci ga kowanne yanki na ƙasar nan – Ministan Yaɗa Labarai

September 1, 2025

An Kama Fitaccen Ɗan Daba da Abokinsa a Kano Saboda Bidiyon Nuna Makamai da Yaɗu Sosai

August 28, 2025
Connect with us
  • Facebook
  • Twitter
  • YouTube
  • WhatsApp
  • Instagram
  • TikTok
Top Posts
Advertisement
© 2026 ASRAH 24 MEDIA. Developed by ENGRMKS & CO..
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.