Babu wani yanki a Arewacin Nijeriya da ya ke da kyakkyawan labarin zaman lafiya, kama da ga Arewa-Maso-Yamma, Arewa-Maso-Gabas ko Arewa-ta-Tsakiya, duba da sauran yankunan Nijeriya da suke zaman lafiya. Zaman lafiyar ke sake bunkasa musu arzukan su.
A wannan lokacin da a ke ganin gangar siyasa ta soma bugawa, harma mutanen yankin sun soma kokawa a game da wariyar da gwamnatin Tinubu take yiwa yankin ta fuskar nade nade da ma aiyukan raya kasa, uwa uba da ko in kula na gaya a game da halin da suke ciki na asarar rayukan su da dukiyoyin su.
Taron kwana biyu na Gwamnatin Tinubu da al’umar Arewa da ya gabata a Kaduna, kusan an yi shine don a warware wa mutanen yankin irin aiyukan da gwamnatin ta yiwa yankin, da kuma sake alkarwanta musu wasu aiyukan da za a yi musu a nan gaba.
Amma fa duk aiyukan da a kace za a yi dama wanda a kayi duk ba su kai a samar musu da zaman lafiya ba, ta yadda za su ci gaba da rayuwar su kamar kowa, suyi sana’oinsu da noman su, su sami damar fita daga kangin da suke ciki na talauci da tashin hankali.
Duk da cewar Shugaba Tinubu ya gaji wannan matsalar ta ta’addanci da fashin daji tun daga Gwamnatin baya ne, amma dole nauyin a yanzu yana wuyan sa, kamar yadda ya ke fada.
Kawo karshen ta’addanci da rashin tsaro a Arewacin Nijeriya zai maida Shugaba Tinubu wani Shugaba na daban tamkar waliyi da ya kawo karshen wani al’amari da ya gagari shugabannin baya, harma da shugaban da ya fito daga yankin.
Samar da tsaro da kawo karshen ta’addanci a Arewacin Nijeriya zai rage kawo karshen talaucin da yake damun yankin.
Samar da tsaro a yankin zai bunkasa noman a Arewacin Nijeriya kuma ya bunkasa tattalin arzikin kasar.
Samar da tsaro a Arewacin Nijeriya zai jawowa Shugaba Tinubu farin jini da ma Jama’iyar sa ta APC.
A yanzu babban muhimmin abin da Arewacin Nijeriya ke bukata bai wuci a kawo musu zaman lafiya ba.