Buba Galadima ya ce zai yi wahalar gaske Kwankwaso ya haɗa hannu da jam’iyyar APC domin samun nasarar Bola Tinubu a babban zaɓen shekarar 2027.Buba Galadima ya bayyana haka ne a tattaunawarsa da tashar Channels a shirinta na Politics Today wanda aka yi a ranar Litinin, inda ya ce gwamnatin Tinubu tana takalar Kwankwaso, musamman wajen goyon bayan Sarki Aminu Ado Bayero, duk da gwamnatin jihar ƙarƙashin Abba Kabir Yusuf ta cire shi.
Da aka tambaye shi cewa akwai yiwuwar NNPP ta haɗu da APC, sai ya ce, “ni yanzu ma nake jin wannan maganar. Kwankwaso ne ɗan siyasar mai ƙarfin tsaya da ƙafarsa saboda ya ja daga a APC a Kano kuma ya doke ta,” in ji shi, inda ya ƙara da cewa shi dai Kwankwaso bai faɗa masa cewa zai mara wa Tinubu baya ba a zaɓen 2027.
Fitaccen ɗansiyasar, ya ce zai so a ce dukkan ƴansiyasar Najeriya za su zama kamar Kwankwaso.
Da aka ce masa wataƙila ana maganar haɗewar Kwankwaso da Tinubu amma bai sani ba, sai ya ce, “Na san da a ce wani ya same shi, sun yi maganar, da dole zan sani. Ba dole ba ne in zama wanda ya fi zama na kusa da shi, amma a siyasa, muna magana da shi sosai, amma kuma bai faɗa min wannan maganar ba.”
Buba Galadima ya ce zai yi wahalar gaske Kwankwaso ya haɗa hannu da jam’iyyar APC domin samun nasarar Bola Tinubu a babban zaɓen shekarar 2027.