Close Menu
  • Home
  • News
    • National
    • International
  • Asrah 24 TV
  • Education
  • Health
  • Podcast
  • Politics
  • Sports
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
Facebook X (Twitter) YouTube WhatsApp Telegram
Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
ASRAH 24 MEDIA
Subscribe
  • Home
  • News
    1. National
    2. International
    3. View All

    Najeriya Ta Kai Dala $18.4 Biliyan a Cinikayyar Cikin Afirka a 2024

    June 28, 2025

    Afreximbank Ta Ba Najeriya Tallafin $50 Biliyan Don Manyan Ayyuka

    June 28, 2025

    Mutane 28 sun mutu sakamakon gudun wuce sa’a a jihar Ondo- FRSC

    February 2, 2025

    Najeriya Ta Fuskanci Limit na Visa zuwa Amurka – 3 Mako Kaɗai!

    July 9, 2025

    Gwamnatin Tarayya Tare da Faransa Za Su Inganta ICT a Jami’o’in Najeriya da Tallafin Naira Biliyan 38

    July 4, 2025

    Zafin Rana Mai Tsanani Ya Ɓarke a Turai: Matsalar Heat Dome

    June 30, 2025

    Najeriya Ta Samu Jarin Waje Har Dala Biliyan 2.5 Daga Masarautar Saudiyya

    June 29, 2025

    Jihohi sun raba Naira biliyan 22.9 a matsayin kudin gyaran muhalli

    September 1, 2025

    Gwamna Bago Ya Rusa Majalisar Ministocinsa a Neja

    September 1, 2025

    Atiku Ya Bukaci Jam’iyyun Adawa Su Ƙi Karɓar Sakamakon Zaɓen Rivers

    September 1, 2025

    Tinubu ya na adalci ga kowanne yanki na ƙasar nan – Ministan Yaɗa Labarai

    September 1, 2025
  • Asrah 24 TV
  • Education

    Ƴar Najeriya ta lashe gasar iya Turanci ta duniya a London

    August 5, 2025

    Yan Kano 3 Sun Yi Nasarar Lashe Gasar Nazarin Tarihin Shehu Usman Dan Fodio A Najeriya Wani gagarumin farin ciki ya bayyana a jihar Kano bayan dalibai uku daga makarantar Rumfa College suka lashe gasar kasa ta nazarin tarihin Shehu Usman Dan Fodio da aka gudanar a Abuja. Gasar wadda ta haɗa jihohi 17 na Arewa, ta nuna hazakar matasan Kano inda suka samu kashi 96% na maki gabaɗaya. > “Mun yi nasara ne saboda muna jin dadin tarihinmu. Shehu Dan Fodio ya ba mu abin alfahari,” in ji ɗaya daga cikin daliban da suka yi nasara. Gwamnatin Kano ta sha alwashin ba su kyautar karatu da tallafi na musam

    August 1, 2025

    NSUBEB ta Bukaci ‘Yan NYSC su Auri Mutane a Jihar Nasarawa

    July 10, 2025

    Ɗalibar Najeriya Ta Lashe Gwarzon Daliba A Oxford

    June 29, 2025

    Gwamnatin Kano ta baiwa dalibai hutun bikin Sallah Babba

    June 1, 2025
  • Health

    WHO Ta Tabbatar Da Sabon Magani Mai Karfi Akan Ciwon Sikila da Sankarau

    June 29, 2025

    Gwamnatin Najeriya za ta fara bada agajin gaggawa kyauta ga marasa Lafiya a Kano

    May 17, 2025

    Cutar Zazzabin Lassa Ta Hallaka Mutane 80 a Najeriya Cikin Mako Daya

    February 25, 2025

    Mutane 28 sun mutu sakamakon gudun wuce sa’a a jihar Ondo- FRSC

    February 2, 2025
  • Podcast
  • Politics

    Gwamnatin Kano Ta Kaddamar da Yakin Kakkabe Malaria

    July 30, 2025

    Keyamo ya Caccaki Atiku kan Sauya Sheka a Lokacin Makokin Rasuwar Buhari

    July 17, 2025

    Gwamna Abba Yusuf Ya Nada Sabon Chief of Staff da DG Special Services

    July 13, 2025

    Gwamnatin Kano Na Neman Ƙara Jiha Guda da Kananan Hukumomi 26

    July 13, 2025

    Yabo Gagarumi Ga Gwamna Abba Yusuf Kan Tsare-Tsaren Hajjin Bana

    July 13, 2025
  • Sports

    Ahmed Musa Ya Yi Alkawarin Dawo da Kano Pillars Zuwa Matsayinta na Gaba da Gaba a Afrika

    July 10, 2025

    Tsohon Goalkeeper Peter Rufai Ya Rasu

    July 4, 2025

    Najeriya ta doke kasar Egyp da ci 4-1: U-20 AFCON

    May 19, 2025

    FIFA ta amince da kasashe 48 su halarci gasar cin kofin Duniya ta Mata a shekarar 2031

    May 10, 2025

    Flying Eagles ta doke kasar Egyp a shirye-shiryen fara tun karar gasar AFCON

    April 23, 2025
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
ASRAH 24 MEDIA
Home » Gwamnatin Neja ta nemi sulhu da gidan rediyon Badeggi FM
News

Gwamnatin Neja ta nemi sulhu da gidan rediyon Badeggi FM

Asrah24 MediaBy Asrah24 MediaAugust 13, 20253 Mins Read
Facebook Twitter WhatsApp

IMG 2938Gwamnatin jihar Neja ta amince da sulhun bayan fage a maimakon shiga kotu da gidan rediyon Badeggi (90.1 FM Radio Station) – kafar yaɗa labarai mai zaman kansa da ke garin Minna – wanda gwamnan jihar Neja, Mohammed Bago, ya ba da umarnin rufewa.

Kafar yaɗa labaran ta shigar da gwamnatin jihar ƙara a gaban kotu kwanaki biyar bayan tilasta mata rufe gidan rediyon a ranar 5 ga Agusta ta hannun lauyanta mai suna, Philip Emmanuel.

A ranar Litinin, a lokacin zaman kotu kan shari’a mai lamba NSHCM/0296/2025 a gaban babbar kotun Minna mai lamba 4, inda lauyan gwamnati Jacob Usman ya sanar da cewa gwamnati tana son tattaunawa a wajen kotu domin sulhuntawa da gidan rediyon.

Usman ya bayyana wa kotun cewa ya tattauna da lauyan waɗanda suka shigar da ƙara domin warware matsalar saboda samun zaman lafiya albarkacin al’ummar jihar Neja.

Ya kuma bayyana wa kotun cewa ya riga ya sanar da mista Emmanuel cewa babban antoni-janar na jihar Neja ya amince ya warware matsalar a wajen kotu.

Mista Emmanuel daga baya ya tabbatar wa da ‘yan jarida cewa, “mun zaɓi ranar 3 ga Satumbar 2025 domin tattaunawa a wajen kotun.”

Mai shari’a, Mohammed Mohammed, a ranar 5 ga Agusta, ya amince da roƙon da mai shigar da ƙara gidan rediyon Badeggi Broadcasting Service Ltd, da manajin-daraktan Mohammed Badeggi.

A cikin hukuncin da ya yanke, mai shari’a Mohammed, ya dakatar da gwamnan jihar da antoni-janar da hukumar bunƙasa birane ta jihar daga ɗaukar mummunan mataki da ka iya shafar lasisin gidan rediyon da ginin gidan yaɗa labaran da ke harabar gidan NTA da ke saman dutsen Minna.

PREMIUM TIMES ta rawaito yadda gwamna Bago ya ba da umarnin rufe gidan rediyon Badeggi FM saboda zargin ƙoƙarin haifar da husuma.

Gwamnan ya ba da umarnin ne a lokacin zaman jiga-jigan jam’iyyar APC wanda aka yi a gidan gwamnati da ke Minna.

Ya kuma ce an ɗauki matakin ne saboda irin ayyukan da gidan rediyon ke yi wanda ya saɓa wa ƙa’ida.

Bago ya kuma zargi mamallakin gidan rediyon da ƙoƙarin tunzura al’umma a kan gwamnati inda ya buƙaci a soke lasisin gidan rediyon.

Gwamnan ya kuma ba wa kwamishinan tsaron cikin gida da rundunar ‘yan sanda umarnin rufe gidan rediyon.

Ƙungiyoyin kare haƙƙin bil’adama kamar SERAP da CJID sun yi Alla-wadai da matakin da gwamnan jihar ya ɗauka. Ƙungiyoyin sun kuma zargi gwamnan da ƙoƙarin murƙushe kafafen yaɗa labarai da tauye ‘yancin faɗar albarkacin baki a jihar.

Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp
Previous ArticleEFCC ta ba da belin tsohon gwamnan Sokoto Waziri Tambuwal da ta tsare
Next Article Gwamnatin Najeriya ta yi maraba da naɗin Maryam Bukar-Hassan a matsayin jakadiyar zaman lafiya ta duniya

Related Posts

Jihohi sun raba Naira biliyan 22.9 a matsayin kudin gyaran muhalli

September 1, 2025

Gwamna Bago Ya Rusa Majalisar Ministocinsa a Neja

September 1, 2025

Atiku Ya Bukaci Jam’iyyun Adawa Su Ƙi Karɓar Sakamakon Zaɓen Rivers

September 1, 2025

Tinubu ya na adalci ga kowanne yanki na ƙasar nan – Ministan Yaɗa Labarai

September 1, 2025
Add A Comment
Leave A Reply Cancel Reply

Latest Posts

Jihohi sun raba Naira biliyan 22.9 a matsayin kudin gyaran muhalli

September 1, 2025

Gwamna Bago Ya Rusa Majalisar Ministocinsa a Neja

September 1, 2025

Atiku Ya Bukaci Jam’iyyun Adawa Su Ƙi Karɓar Sakamakon Zaɓen Rivers

September 1, 2025

Tinubu ya na adalci ga kowanne yanki na ƙasar nan – Ministan Yaɗa Labarai

September 1, 2025

An Kama Fitaccen Ɗan Daba da Abokinsa a Kano Saboda Bidiyon Nuna Makamai da Yaɗu Sosai

August 28, 2025
Connect with us
  • Facebook
  • Twitter
  • YouTube
  • WhatsApp
  • Instagram
  • TikTok
Top Posts
Advertisement
© 2026 ASRAH 24 MEDIA. Developed by ENGRMKS & CO..
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.