Alhaji Aminu Alhassan Dantata dai ya yi karatunsa na share fage daga 1938 zuwa 1945 a makarantar Firamare ta Dala, kuma ya halarci Makarantar Turanci da Larabci ta Dantata tsakanin 1945 zuwa 1949.
Mahaifinsa, Alhassan Dantata, an haife shi a shekara ta 1877 kuma ya rasu a ranar 17 ga watan Agustan, 1955, ɗan kasuwa ne a fannin kayayyakin amfanin gona, wanda ke tallata hajarsa kasashe daban daban na Duniya.
Marigayi Aminu Dantata ya yi saurin koyi da kasuwancin mahaifinsa kuma ya yi fice sosai a fagen kasuwancin.
Ya fara harkokinsa na kasuwanci a matsayin mai siyen kayayyaki ya siyar a shekarar 1949 a kasuwancin dangin kamfanin Alhassan Dantata and Sons Limited, ya zama Shugaba kuma Manajan Daraktan Kamfanin a 1960.
Ya kasance memba na Kwamitin Gudanarwa na Bankin bunkasa Masana’antu na Najeriya, ya kuma zama Daraktan Bankin tsakanin 1962 zuwa 1966.
Alhaji Aminu Dantata shi ne wanda ya kafa kamfanin Express Petroleum and Gas Company Limited kuma yana daga cikin mutanen da suka jagoranci Bankin Jaiz a kasar nan.
Fitaccen dan kasuwar dai ya jagoranci ayyukan kasuwanci da yawa zuwa ƙasashe daban daban na Duniya.
A wata hira da akai dashi lokacin yana Raye a matsayinsa na wanda ya kafu a harkar kasuwanci, Alhaji Aminu Dantata ya yi imanin cewa kasuwanci yana da maganin rashin zaman lafiya da rashin aikin yi.
A cewar sa sai anyi kasuwanci za a samu masana’antu kuma mutane za su sami kwanciyar hankali a harkokin kasuwancinsu, kuma shugabanni za su mallaki talakawansu kuma su bunkasa al’umma a dukkan matakai.
Alhaji Aminu Dantata baya ga manyan nasarori da ya samu a kasuwanci ya kuma jefa ƙafafun sa a harkar siyasa a cikin kasar nan kasancewarsa ɗan majalisar wakilai na lokaci ɗaya a jihar Kaduna a lokacin Jamhuriya ta Farko, sannan kuma ya kasance mamba a majalisar lardin Kano.
Ya kuma taba rike mukamin mamba na sabuwar Jihar Kano da aka kafa a shekarar 1967, inda ya yi aiki a matsayin kwamishinan kasuwanci da masana’antu na jihar a karkashin marigayi Audu Bako, gwamnan Kano a lokacin gwamnatin soja ta Janar Yakubu Gowon.
Gabanin Jamhuriya ta Biyu, wacce ta samar da marigayi Alhaji Shehu Shagari a matsayin shugaban kasa, Alummar kasar nan daga sassa daban daban sunta kiraye-kiraye kan ya fito takarar shugabancin Najeriya sai dai yayi watsi da kiran nasu inda bai fitoba.
Ana dai kallon Marigayi Aminu Dantata a matsayin daya daga cikin mawadata mafi alkhairi a kasar nan, wanda kyautatawarsa ya canza rayuwar mutane da dama.
Alhaji Aminu ne ɗa na ƙarshe wanda ke da rai a cikin ‘ya’yan Alhaji Alhassan Dantata.
Alhaji Aminu Alhassan Dantata dai ya rasu da Asubahin yau a birnin Abu Dhabi na Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, yana da shekara 94 a Duniya.
Aminu Dantata, kawu ne ga shahararren mai kuɗin nan na Afirka Alhaji Aliko Dangote.
