Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa sauye-sauyen tattalin arzikin da gwamnatinsa ke aiwatarwa suna nufin gyara makomar matasan da ke tasowa a Najeriya.
Da yake jawabi ga ƙungiyar ‘yan majalisa ta Jamhuriya ta Uku, wadda ya kasance cikin ta a baya, Tinubu ya ce a cikin shekaru 50 da suka gabata, Najeriya tana kashe kuɗaɗen yaran da ba a haihuwarsu ba, tare da dogaro da man fetur wajen samun kudin shiga.
Ya kuma bayyana matsalolin da ya fuskanta a farkon mulkinsa, musamman a fannin tattalin arziki, yana mai cewa matakan da ya dauka ne suka hana Najeriya durkushewa.
Tinubu ya kara da cewa yanzu ana fara ganin amfanin manufofin gwamnatinsa, yana mai cewa farashin abinci ya fara raguwa, sannan darajar Naira ta daidaita a kasuwannin ketare.
